scripture.how 聖書写経
JA

Copywork

Hausa BSRK Acts 16장

写経は速く終える入力練習ではなく、一節ずつみ言葉の文と流れを改めて受け止める時間です。入力内容はこのブラウザに一時保存され、ログインするとアカウントにも保存されます。

KO 韓国語
ZH 中国語
JA 日本語
HI ヒンディー語
BN ベンガル語
TA タミル語
TE テルグ語
ML マラヤーラム語
FA ペルシア語
MY ビルマ語
NE ネパール語
MR マラーティー語
KN カンナダ語
HA ハウサ語
YO ヨルバ語
SW スワヒリ語
IG イボ語
ID インドネシア語
TSI
PT ポルトガル語
VI ベトナム語
AR アラビア語
AVD
RU ロシア語
UK ウクライナ語
RO ルーマニア語
BTF
IT イタリア語
FI フィンランド語
TO トンガ語
HR クロアチア語
SR セルビア語
TR トルコ語
HU ハンガリー語
PL ポーランド語
SK スロバキア語
LA ラテン語
NL オランダ語
CS チェコ語
FR フランス語
ES スペイン語
DE ドイツ語
ETC その他の言語

小見出し単位で進める · Acts

1:1-5 Preface to Theophilus 1:6-11 The Ascension of Jesus and the Promise of His Return 1:12-14 The Disciples Devoted to Prayer in the Upper Room 1:15-26 Matthias Chosen to Replace Judas 2:1-13 The Holy Spirit Comes at Pentecost 2:14-36 Peter Addresses the Crowd 2:37-41 Three Thousand Repent and Are Baptized 2:42-47 The Fellowship of the First Believers 3:1-10 Peter Heals the Lame Beggar at the Temple Gate 3:11-26 Peter Preaches in Solomon's Portico 4:1-12 Peter and John Before the Council 4:13-22 The Rulers Forbid Preaching in Jesus' Name 4:23-31 The Believers Pray for Boldness 4:32-37 The Community That Shared All Things 5:1-11 The Deceit and Death of Ananias and Sapphira 5:12-16 Signs and Wonders Through the Apostles 5:17-26 The Apostles Imprisoned and Freed by an Angel 5:27-33 The Apostles Obey God Rather Than Men 5:34-42 Gamaliel's Counsel and the Apostles Beaten 6:1-7 Seven Chosen to Serve 6:8-15 Stephen Seized and Brought Before the Council 7:1-8 Stephen Recounts the Call of Abraham 7:9-19 Joseph and the Ancestors in Egypt 7:20-29 The Birth of Moses and His Flight to Midian 7:30-43 Israel's Rebellion in the Wilderness 7:44-50 The Folly of Trusting in a House Made by Hands 7:51-60 The Stoning of Stephen 8:1-8 The Scattered Believers Spread the Gospel 8:9-25 Simon the Magician Rebuked 8:26-40 Philip and the Ethiopian Eunuch 9:1-9 Saul Meets the Risen Lord on the Road to Damascus 9:10-19 Saul's Sight Restored Through Ananias 9:20-31 Saul Preaches Boldly in Damascus and Jerusalem 9:32-35 Peter Heals Aeneas at Lydda 9:36-43 Peter Raises Tabitha at Joppa 10:1-8 The Vision of Cornelius the Devout Centurion 10:9-23 Peter's Vision of the Sheet 10:24-33 Peter Enters the House of Cornelius 10:34-43 Salvation Comes to the Gentiles 10:44-48 The Holy Spirit Poured Out on the Gentiles 11:1-18 Peter Explains Himself in Jerusalem 11:19-26 First Called Christians at Antioch 11:27-30 Relief Sent to the Brethren in Judea 12:1-5 The Martyrdom of James and the Imprisonment of Peter 12:6-19 An Angel Leads Peter Out of Prison 12:20-25 The Wretched End of the Proud Herod 13:1-3 Barnabas and Saul Sent Off 13:4-12 Paul Rebukes the Magician in Cyprus 13:13-41 Paul Preaches in the Synagogue at Pisidian Antioch 13:42-52 The Two Apostles Turn to the Gentiles 14:1-7 Preaching and Division at Iconium 14:8-20 The Apostles Mistaken for Gods at Lystra 14:21-28 Strengthening the Churches and Returning to Antioch 15:1-5 The Dispute Over Circumcision 15:6-21 The Council at Jerusalem 15:22-35 The Letter of Decision Sent to the Gentile Churches 15:36-41 Paul and Barnabas Part Ways 16:1-5 Paul Takes Timothy as a Companion 16:6-10 The Vision to Come Over to Macedonia 16:11-15 Lydia Believes at Philippi 16:16-24 Healing the Slave Girl and Imprisonment 16:25-40 The Prison Doors Open and the Jailer Is Saved 17:1-9 Preaching and Uproar at the Thessalonian Synagogue 17:10-15 The Bereans Examine the Scriptures 17:16-34 Paul Preaches at the Areopagus in Athens 18:1-11 Aquila and Priscilla Met at Corinth 18:12-17 Paul Brought Before Gallio 18:18-23 Returning to Antioch and Setting Out Again 18:24-28 Apollos Instructed at Ephesus 19:1-7 The Disciples at Ephesus Receive the Holy Spirit 19:8-12 Continued Teaching in the Hall of Tyrannus 19:13-20 The Exorcists and the Burning of Magic Books 19:21-41 The Riot Stirred Up by Demetrius the Silversmith 20:1-6 Through Macedonia and Greece to Troas 20:7-12 Eutychus Restored to Life at Troas 20:13-16 The Voyage to Miletus 20:17-38 Paul's Farewell to the Ephesian Elders 21:1-16 The Final Voyage to Jerusalem 21:17-26 Paul Meets James and Observes the Rite of Purification 21:27-40 Paul Arrested in the Temple 22:1-21 Paul Testifies to His Conversion Before the Crowd 22:22-29 Spared the Scourge by Roman Citizenship 22:30 Paul Brought Before the Council 23:1-11 The Argument That Divided Pharisees and Sadducees 23:12-22 The Plot to Kill Paul 23:23-35 Paul Sent Under Guard to the Governor at Caesarea 24:1-9 The Accusation Before Felix 24:10-21 Paul's Defense Before Felix 24:22-27 Felix Keeps Paul in Custody 25:1-12 Paul Appeals to Caesar 25:13-27 Festus Lays the Case Before Agrippa 26:1-11 Paul Recounts His Former Life Before Agrippa 26:12-23 Paul Testifies to the Heavenly Commission 26:24-32 Paul's Appeal to the King 27:1-12 The Beginning of the Voyage to Rome 27:13-26 The Ship Caught in the Storm 27:27-38 Salvation Promised to the Crew and Passengers 27:39-44 The Ship Wrecked and All Are Saved 28:1-10 Kindness Shown on the Island of Malta 28:11-16 Paul Arrives at Last in Rome 28:17-29 Paul's Testimony to the Jews in Rome 28:30-31 Boldly Proclaiming the Kingdom of God
16:1
待機

Bulus ya kai Derbe sa’an nan kuma zuwa Listira, inda wani almajiri mai suna Timoti yake da zama, wanda mahaifiyarsa mutuniyar Yahuda ce kuma mai bi ce, amma mahaifinsa mutumin Hellenawa ne.

16:2
待機

’Yan’uwa a Listira da Ikoniyum sun yi magana mai kyau ƙwarai a kansa.

16:3
待機

Bulus ya so ya ɗauke shi a tafiyar, saboda haka ya yi masa kaciya, domin Yahudawan da suke da zama a wurin, don duk sun san cewa mahaifinsa mutumin Hellenawa ne.

16:4
待機

Yayinda suke tafiya daga gari zuwa gari, suka dinga ba da shawarwarin da manzanni da dattawa a Urushalima suka zartar domin mutane su kiyaye.

16:5
待機

Saboda haka ikkilisiyoyi suka ginu cikin bangaskiya suka kuma yi girma suka yi ta ƙaruwa kowace rana.

16:6
待機

Bulus da abokan tafiyarsa suka zazzaga dukan yankin Firjiya da Galatiya, don Ruhu Mai Tsarki ya hana su yin wa’azi a lardin Asiya.

16:7
待機

Da suka isa kan iyakar Misiya, suka yi ƙoƙari su shiga Bitiniya, amma Ruhun Yesu bai yarda musu ba.

16:8
待機

Saboda haka suka ratsa Misiya suka zo Toruwas.

16:9
待機

Da dare Bulus ya ga wahayin wani mutumin Makidoniya yana tsaye yana roƙonsa cewa, “Ka zo Makidoniya ka taimake mu.”

16:10
待機

Bayan Bulus ya ga wahayin, muka shirya nan take mu tashi zuwa Makidoniya, mun tabbata cewa, Allah ya kira mu mu yi musu wa’azin bishara.

16:11
待機

Daga Toruwas muka tashi zuwa teku muka kuma shiga jirgin ruwa muka miƙe kai tsaye zuwa Samotiras, kashegari kuma muka nufi Neyafolis.

16:12
待機

Daga can muka tafi Filibbi, wata babbar alkaryar Roma wadda kuma take babban birni a gundumar Makidoniya. Muka zauna a can kwanaki masu yawa.

16:13
待機

A Asabbaci, muka fita ƙofar birnin zuwa bakin kogi, inda muke tsammani za mu sami wurin yin addu’a. Muka zauna muka fara yin wa matan da suka taru a can magana.

16:14
待機

Ɗaya daga cikin waɗanda suka saurare mu mace ce mai suna Lidiya, mai sayar da yadunan jan garura masu tsada daga birnin Tiyatira, mai yi wa Allah sujada. Ubangiji ya buɗe zuciyarta har ta karɓi saƙon Bulus.

16:15
待機

Da aka yi mata baftisma tare da iyalin gidanta, sai ta gayyace mu zuwa gidanta. Ta ce, “In kun amince ni mai bi ce cikin Ubangiji, sai ku zo ku sauka a gidana.” Sai ta kuwa rinjaye mu.

16:16
待機

Wata rana muna tafiya zuwa wurin yin addu’a, sai muka sadu da wata baranya mai ruhun aljani mai duba. Takan samo wa mutanenta kuɗi da yawa, duban da take yi.

16:17
待機

Wannan yarinya kuwa ta bi Bulus da kuma sauranmu, tana ihu tana cewa, “Waɗannan mutane bayin Allah Mafi Ɗaukaka ne, suna sanar da ku hanyar ceto.”

16:18
待機

Ta yi ta faɗin haka har kwanaki masu yawa. A ƙarshe Bulus ya damu ƙwarai sai ya juya ya ce wa aljanin, “A cikin sunan Yesu Kiristi na umarce ka, ka rabu da ita!” Nan take aljanin ya rabu da ita.

16:19
待機

Da iyayengijin baranyar suka ga hanyar samun kuɗinsu ta toshe, sai suka kama Bulus da Sila suka ja su zuwa cikin kasuwa don su fuskanci hukuma.

16:20
待機

Sai suka kawo su a gaban alƙalai suka ce, “Waɗannan Yahudawa ne, suna kuma birkitar mana da gari,

16:21
待機

ta wurin koyar da al’adun da ba daidai ba ne mu Romawa mu karɓa ko mu aikata.”

16:22
待機

Sai taron suka fāɗa wa Bulus da Sila gaba ɗaya, alƙalan kuwa suka yi umarni a tuɓe su a kuma yi musu dūka.

16:23
待機

Bayan an yi musu bulala sosai, sai aka jefa su cikin kurkuku, aka umarci mai gadin kurkukun yă tsare su da kyau.

16:24
待機

Da karɓan irin umarnan nan, sai ya sa su can cikin ɗakin kurkuku na ciki-ciki, kuma ya ɗaura ƙafafunsu a turu.

16:25
待機

Wajen tsakar dare Bulus da Sila suna addu’a suna rera waƙoƙi ga Allah, sauran ’yan kurkuku kuwa suna sauraronsu.

16:26
待機

Ba zato ba tsammani sai aka yi wata babbar girgizar ƙasa har tushen ginin kurkukun ya jijjiga. Nan da nan sai duk ƙofofin kurkukun suka bubbuɗe, sarƙoƙin kowa kuma suka ɓaɓɓalle.

16:27
待機

Mai gadin kurkukun ya farka daga barci, sa’ad da ya ga ƙofofin kurkukun a buɗe, sai ya zāre takobinsa yana shirin kashe kansa domin ya ɗauka ’yan kurkukun sun gudu.

16:28
待機

Amma Bulus ya yi ihu ya ce, “Kada ka yi wa kanka lahani! Dukanmu muna nan!”

16:29
待機

Mai gadin kurkukun ya kira a kawo fitilu, ya ruga ciki ya fāɗi yana rawan jiki a gaban Bulus da Sila.

16:30
待機

Sai ya fito da su waje ya kuma tambaye su ya ce, “Ranku yă daɗe, me zan yi domin in sami ceto?”

16:31
待機

Suka amsa suka ce, “Ka gaskata da Ubangiji Yesu, za ka sami ceto, kai da iyalinka.”

16:32
待機

Sa’an nan suka yi masa maganar Ubangiji shi da kuma dukan sauran da suke a gidansa.

16:33
待機

A wannan sa’a na daren, mai gadin kurkukun ya ɗauke su ya wanke musu raunukansu; nan take aka yi masa baftisma da dukan iyalinsa.

16:34
待機

Sai mai gadin kurkukun ya kawo su cikin gidansa ya ba su abinci; ya kuwa cika da murna don yă gaskata da Allah, shi da dukan iyalinsa.

16:35
待機

Da gari ya waye, sai alƙalan suka aika ma’aikatansu wajen mai gadin kurkukun da umarni cewa, “Ka saki mutanen nan.”

16:36
待機

Sai mai gadin kurkukun ya gaya wa Bulus cewa, “Alƙalai sun ba da umarni a sake ku kai da Sila. Yanzu sai ku tafi. Ku sauka lafiya.”

16:37
待機

Amma Bulus ya ce wa ma’aikatan, “Sun yi mana dūka a fili ba tare da shari’a ba, ko da yake mu ’yan ƙasar Roma ne, suka kuma jefa mu cikin kurkuku. Yanzu suna so su fitar da mu a ɓoye? A’a! Sai dai su zo da kansu su rako mu waje.”

16:38
待機

Sai ma’aikatan suka faɗa wa alƙalan wannan, da suka ji cewa Bulus da Sila Romawa ne, sai suka ji tsoro.

16:39
待機

Sai suka zo don su roƙe su, suka yi musu rakiya daga kurkukun, suna roƙonsu su bar birnin.

16:40
待機

Bayan Bulus da Sila suka fita daga kurkukun, sai suka tafi gidan Lidiya, inda suka sadu da ’yan’uwa suka kuma ƙarfafa su. Sa’an nan suka tafi.