scripture.how 聖書写経
JA

Copywork

Hausa BSRK Luke 2장

写経は速く終える入力練習ではなく、一節ずつみ言葉の文と流れを改めて受け止める時間です。入力内容はこのブラウザに一時保存され、ログインするとアカウントにも保存されます。

KO 韓国語
ZH 中国語
JA 日本語
HI ヒンディー語
BN ベンガル語
TA タミル語
TE テルグ語
ML マラヤーラム語
FA ペルシア語
MY ビルマ語
NE ネパール語
MR マラーティー語
KN カンナダ語
HA ハウサ語
YO ヨルバ語
SW スワヒリ語
IG イボ語
ID インドネシア語
TSI
PT ポルトガル語
VI ベトナム語
AR アラビア語
AVD
RU ロシア語
UK ウクライナ語
RO ルーマニア語
BTF
IT イタリア語
FI フィンランド語
TO トンガ語
HR クロアチア語
SR セルビア語
TR トルコ語
HU ハンガリー語
PL ポーランド語
SK スロバキア語
LA ラテン語
NL オランダ語
CS チェコ語
FR フランス語
ES スペイン語
DE ドイツ語
ETC その他の言語

小見出し単位で進める · Luke

1:1-4 Dedication to Theophilus 1:5-25 The Birth of John the Baptist Foretold 1:26-38 The Birth of Jesus Foretold 1:39-45 Mary Visits Elizabeth 1:46-56 Mary's Song of Praise: The Magnificat 1:57-66 The Birth of John the Baptist 1:67-80 Zechariah's Prophecy 2:1-7 The Birth of Jesus in Bethlehem 2:8-20 The Shepherds and the Angels 2:21-24 Jesus Presented in the Temple 2:25-35 Simeon Holds the Child 2:36-40 The Testimony of the Prophetess Anna 2:41-52 The Boy Jesus in the Temple 3:1-14 John the Baptist Prepares the Way 3:15-17 The Testimony of John the Baptist 3:18-20 John the Baptist Imprisoned 3:21-22 The Baptism of Jesus 3:23-38 The Genealogy of Jesus 4:1-13 The Temptation of Jesus 4:14-30 Jesus Rejected at Nazareth 4:31-37 Jesus Drives Out an Unclean Spirit 4:38-39 Jesus Heals Peter's Mother-in-Law 4:40-44 Jesus Heals Many and Withdraws to Pray 5:1-11 The Miraculous Catch of Fish 5:12-16 Jesus Cleanses a Leper 5:17-26 Jesus Heals a Paralytic 5:27-32 Jesus Calls Levi the Tax Collector 5:33-39 The Question About Fasting and New Wine 6:1-5 Jesus Is Lord of the Sabbath 6:6-11 Jesus Heals a Man with a Withered Hand on the Sabbath 6:12-16 Jesus Chooses the Twelve Apostles 6:17-26 Blessings and Woes on the Plain 6:27-36 Love Your Enemies 6:37-42 Do Not Judge 6:43-45 A Tree Is Known by Its Fruit 6:46-49 The House Built on the Rock 7:1-10 The Faith of the Centurion 7:11-17 Jesus Raises the Widow's Son at Nain 7:18-35 The Question of John the Baptist 7:36-50 A Sinful Woman's Love and Forgiveness 8:1-3 The Women Who Served Jesus 8:4-8 The Parable of the Sower 8:9-15 The Parable of the Sower Explained 8:16-18 A Lamp on a Stand 8:19-21 Jesus' True Family 8:22-25 Jesus Calms the Storm 8:26-39 Jesus Heals a Demon-Possessed Man at Gerasa 8:40-56 Jairus's Daughter and the Woman with the Issue of Blood 9:1-6 Jesus Sends Out the Twelve 9:7-9 Herod Hears About Jesus 9:10-17 Jesus Feeds the Five Thousand 9:18-21 Peter's Confession of Faith 9:22-27 Jesus Foretells His Suffering 9:28-36 The Transfiguration 9:37-43 Jesus Heals a Boy with an Unclean Spirit 9:44-45 Jesus Again Foretells His Death 9:46-50 Who Is the Greatest 9:51-56 A Samaritan Village Rejects Jesus 9:57-62 The Cost of Following Jesus 10:1-12 Jesus Sends Out the Seventy-Two 10:13-16 Woes on Unrepentant Towns 10:17-20 The Return of the Seventy-Two 10:21-24 Jesus Rejoices and Gives Thanks 10:25-37 The Parable of the Good Samaritan 10:38-42 Martha and Mary 11:1-13 Jesus Teaches on Prayer 11:14-23 Jesus and Beelzebul 11:24-28 The Generation That Seeks a Sign 11:29-32 The Sign of Jonah 11:33-36 The Lamp of the Body Is the Eye 11:37-54 Woes to the Pharisees and Lawyers 12:1-12 Beware of the Leaven of the Pharisees 12:13-21 The Parable of the Rich Fool 12:22-34 Do Not Be Anxious About Your Life 12:35-48 Watchful Servants 12:49-53 Jesus Came to Bring Division 12:54-59 Interpreting the Present Time 13:1-5 Repent or Perish 13:6-9 The Parable of the Barren Fig Tree 13:10-17 Jesus Heals a Crippled Woman on the Sabbath 13:18-19 The Parable of the Mustard Seed 13:20-21 The Parable of the Leaven 13:22-30 The Narrow Door 13:31-35 Lament Over Jerusalem 14:1-6 Jesus Heals a Man with Dropsy on the Sabbath 14:7-14 The Lesson of the Lowest Place 14:15-24 The Parable of the Great Banquet 14:25-35 The Cost of Discipleship 15:1-7 The Parable of the Lost Sheep 15:8-10 The Parable of the Lost Coin 15:11-32 The Parable of the Lost Son 16:1-13 The Parable of the Dishonest Manager 16:14-18 The Law and the Kingdom of God 16:19-31 The Rich Man and Lazarus 17:1-4 On Temptations to Sin and Forgiveness 17:5-10 Faith Like a Mustard Seed and the Servant's Duty 17:11-19 Jesus Cleanses Ten Lepers 17:20-37 The Coming of the Kingdom of God 18:1-8 The Parable of the Persistent Widow and the Unjust Judge 18:9-14 The Pharisee and the Tax Collector 18:15-17 Jesus Blesses the Little Children 18:18-30 The Rich Ruler 18:31-34 Jesus Foretells His Death a Third Time 18:35-43 Jesus Heals a Blind Beggar at Jericho 19:1-10 Jesus Calls Zacchaeus the Tax Collector 19:11-27 The Parable of the Ten Minas 19:28-40 The Triumphal Entry into Jerusalem 19:41-44 Jesus Weeps Over Jerusalem 19:45-48 Jesus Cleanses the Temple 20:1-8 The Authority of Jesus Questioned 20:9-19 The Parable of the Tenants 20:20-26 Paying Taxes to Caesar 20:27-40 The Question About the Resurrection 20:41-44 Whose Son Is the Christ 20:45-47 Beware of the Scribes 21:1-4 The Widow's Two Coins 21:5-36 The Olivet Discourse: Signs of the End 22:1-6 Judas Plots to Betray Jesus 22:7-13 Preparation of the Passover 22:14-20 The Institution of the Lord's Supper 22:21-23 Jesus Foretells His Betrayal 22:24-30 The Dispute About Who Is the Greatest 22:31-34 Jesus Foretells Peter's Denial 22:35-38 Purse, Bag, and Sword 22:39-46 Jesus Prays on the Mount of Olives 22:47-53 The Betrayal and Arrest of Jesus 22:54-62 Peter Denies Jesus 22:63-71 Jesus Before the Council 23:1-25 Jesus Before Pilate 23:26-43 The Crucifixion 23:44-49 The Death of Jesus 23:50-56 The Burial of Jesus 24:1-12 The Resurrection 24:13-35 On the Road to Emmaus 24:36-49 Jesus Appears to His Disciples 24:50-53 The Ascension
2:1
待機

A waɗancan kwanaki, Kaisar Augustus ya ba da doka cewa ya kamata a yi ƙidaya a dukan masarautar Roma.

2:2
待機

(Wannan ce ƙidaya ta fari da aka yi a lokacin da Kwiriniyus yake gwamnar Suriya.)

2:3
待機

Sai kowa ya koma garinsa don a rubuta shi.

2:4
待機

Saboda haka Yusuf ma ya haura daga Nazaret a Galili zuwa Yahudiya, ya tafi Betlehem garin Dawuda, don shi daga gida da kuma zuriyar Dawuda ne.

2:5
待機

Ya tafi can don a rubuta shi tare da Maryamu, wadda aka yi masa alkawari zai aura, tana kuwa da ciki.

2:6
待機

Yayinda suke can, sai lokacin haihuwar jaririn ya yi,

2:7
待機

ta kuwa haifi ɗanta na fari. Ta nannaɗe shi a zane ta kuma kwantar da shi cikin wani kwami, don ba su sami ɗaki a masauƙi ba.

2:8
待機

Akwai makiyaya masu zama a fili kusa da wurin, suna tsaron garkunan tumakinsu da dare.

2:9
待機

Sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare su, ɗaukakar Ubangiji kuma ta haskaka kewaye da su, suka kuwa tsorata ƙwarai.

2:10
待機

Amma mala’ikan ya ce musu, “Kada ku ji tsoro. Na kawo muku labari mai daɗi na farin ciki mai yawa ne wanda zai zama domin dukan mutane.

2:11
待機

Yau a birnin Dawuda an haifa muku Mai Ceto; shi ne Kiristi Ubangiji.

2:12
待機

Wannan zai zama alama a gare ku. Za ku tarar da jariri a nannaɗe a zane kwance a kwami.”

2:13
待機

Ba labari sai ga taron rundunar sama suka bayyana tare da mala’ikan, suna yabon Allah suna cewa,

2:14
待機

“Ɗaukaka ga Allah a can cikin sama,

2:15
待機

Da mala’ikun suka bar su, su suka koma sama, sai makiyayan suka ce wa juna, “Mu je Betlehem mu ga wannan abin da ya faru, wanda Ubangiji ya sanar mana.”

2:16
待機

Sai suka tafi da sauri, suka tarar da Maryamu da Yusuf, da kuma jaririn kwance a kwami.

2:17
待機

Sa’ad da suka gan shi, sai suka baza maganar da aka gaya musu game da yaron,

2:18
待機

duk kuwa waɗanda suka ji wannan, suka yi mamaki a kan abin da makiyayan suka faɗa.

2:19
待機

Amma Maryamu ta riƙe dukan waɗannan abubuwa ta kuma yi ta tunaninsu a zuciyarta.

2:20
待機

Makiyayan kuwa suka koma, suna ɗaukaka suna kuma yabon Allah saboda dukan abubuwan da suka ji, suka kuma gani, yadda aka gaya musu.

2:21
待機

A rana ta takwas, da lokaci ya yi da za a yi masa kaciya, sai aka ba shi suna Yesu, sunan da mala’ika ya ba shi kafin a yi cikinsa.

2:22
待機

Da lokacin tsarkakewarsu bisa ga Dokar Musa ya cika, sai Yusuf da Maryamu suka ɗauke shi suka haura zuwa Urushalima don su miƙa shi ga Ubangiji

2:23
待機

(yadda yake a rubuce a Dokar Ubangiji cewa, “Kowane ɗan fari, za a keɓe shi ga Ubangiji” ),

2:24
待機

don kuma su miƙa hadaya bisa ga abin da aka faɗa a Dokar Ubangiji cewa, “kurciyoyi biyu ko ’yan tattabarai biyu.”

2:25
待機

To, akwai wani mutum a Urushalima mai suna Siman, shi mai adalci da kuma mai ibada. Yana jiran fansar Isra’ila, Ruhu Mai Tsarki kuwa yana tare da shi.

2:26
待機

An bayyana masa ta wurin Ruhu Mai Tsarki cewa ba zai mutu ba sai ya ga Kiristi na Ubangiji.

2:27
待機

Da Ruhu ya iza shi, sai ya shiga cikin filin haikali. Sa’ad da iyayen suka kawo jaririn nan Yesu don su yi masa abin da al’adar Doka ta bukaci,

2:28
待機

sai Siman ya karɓi yaron a hannuwansa ya yabi Allah, yana cewa,

2:29
待機

“Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kamar yadda ka yi alkawari,

2:30
待機

Gama idanuna sun ga cetonka,

2:31
待機

wanda ka shirya a gaban dukan mutane,

2:32
待機

haske don bayyanawa ga Al’ummai

2:33
待機

Mahaifin yaron da kuma mahaifiyarsa suka yi mamaki abin da aka faɗa game da shi.

2:34
待機

Sa’an nan Siman ya sa musu albarka ya ce wa Maryamu mahaifiyarsa, “An ƙaddara yaron nan yă zama sanadin fāɗuwa da tashin mutane da yawa a Isra’ila, zai kuma zama alamar da mutane ba za su so ba,

2:35
待機

ta haka za a fallasa tunanin zukatan mutane da yawa. Ke ma, takobi zai soki zuciyarki.”

2:36
待機

Akwai wata annabiya ma, mai suna Anna, diyar Fanuwel, na kabilar Asher. Ta tsufa kutuf; ta yi zama da mijinta shekaru bakwai bayan sun yi aure,

2:37
待機

ta kuwa zama gwauruwa sai da ta kai shekaru tamanin da huɗu. Ba ta taɓa barin haikali ba, tana sujada dare da rana, tana kuma azumi da addu’a.

2:38
待機

Tana haurawa wurinsu ke nan a wannan lokaci, sai ta yi wa Allah godiya ta kuma yi magana game da yaron nan ga dukan waɗanda suke sauraron fansar Urushalima.

2:39
待機

Bayan da Yusuf da Maryamu suka gama yin dukan abubuwan da Dokar Ubangiji ta bukaci, sai suka koma Galili suka tafi Nazaret garinsu.

2:40
待機

Yaron kuwa ya yi girma ya yi ƙarfi; ya cika da hikima, alherin Allah kuwa yana bisansa.

2:41
待機

Kowace shekara, iyayen Yesu sukan je Urushalima don Bikin Ƙetarewa.

2:42
待機

Da Yesu ya cika shekaru goma sha biyu, sai suka tafi Bikin bisa ga al’ada.

2:43
待機

Bayan Bikin, da iyayen suka kama hanya don su koma gida, sai Yesu, yaron nan, ya tsaya a Urushalima, ba da saninsu ba.

2:44
待機

Su kuwa sun ɗauka yana tare da su, saboda haka, suka yi ta tafiya har na yini guda. Sa’an nan suka fara nemansa cikin ’yan’uwansu da abokansu.

2:45
待機

Da ba su gan shi ba, sai suka koma Urushalima nemansa.

2:46
待機

Bayan kwana uku, sai suka same shi a filin haikali zaune a tsakiyar malamai, yana sauraronsu yana kuma yi musu tambayoyi.

2:47
待機

Dukan waɗanda suka ji shi, suka yi mamakin fahimtarsa, da amsoshinsa.

2:48
待機

Da iyayensa suka gan shi sai suka yi mamaki. Mahaifiyarsa ta ce masa, “Ɗana, don me ka yi mana haka? Ni da mahaifinka duk mun damu muna nemanka.”

2:49
待機

Sai ya ce, “Don me kuke nemana? Ba ku san cewa, dole in kasance a gidan Ubana ba?”

2:50
待機

Amma ba su fahimci abin da yake faɗin musu ba.

2:51
待機

Sai ya koma Nazaret tare da su, yana yi musu biyayya. Mahaifiyarsa kuma ta riƙe dukan waɗannan abubuwa a zuciyarta.

2:52
待機

Yesu kuwa ya yi girma, ya kuma ƙaru cikin hikima, ya kuma sami tagomashi a wurin Allah da mutane.