scripture.how 성경필사
KO

Copywork

Hausa BSRK 누가복음 10장

성경필사는 빠르게 끝내는 입력 훈련이 아니라, 한 절씩 말씀의 문장과 흐름을 다시 붙드는 시간입니다. 입력 내용은 이 브라우저에 임시 저장되며, 로그인하면 계정에도 저장됩니다.

KO 한국어
ZH 중국어
JA 일본어
HI 힌디어
BN 벵골어
TA 타밀어
TE 텔루구어
ML 말라얄람어
FA 페르시아어
MY 버마어
NE 네팔어
MR 마라티어
KN 칸나다어
HA 하우사어
YO 요루바어
SW 스와힐리어
IG 이그보어
ID 인도네시아어
TSI
PT 포르투갈어
VI 베트남어
AR 아랍어
AVD
RU 러시아어
UK 우크라이나어
RO 루마니아어
BTF
IT 이탈리아어
FI 핀란드어
TO 통가어
HR 크로아티아어
SR 세르비아어
TR 튀르키예어
HU 헝가리어
PL 폴란드어
SK 슬로바키아어
LA 라틴어
NL 네덜란드어
CS 체코어
FR 프랑스어
ES 스페인어
DE 독일어
ETC 기타 언어

소제목 단위로 진행 · 누가복음

1:1-4 Dedication to Theophilus 1:5-25 The Birth of John the Baptist Foretold 1:26-38 The Birth of Jesus Foretold 1:39-45 Mary Visits Elizabeth 1:46-56 Mary's Song of Praise: The Magnificat 1:57-66 The Birth of John the Baptist 1:67-80 Zechariah's Prophecy 2:1-7 The Birth of Jesus in Bethlehem 2:8-20 The Shepherds and the Angels 2:21-24 Jesus Presented in the Temple 2:25-35 Simeon Holds the Child 2:36-40 The Testimony of the Prophetess Anna 2:41-52 The Boy Jesus in the Temple 3:1-14 John the Baptist Prepares the Way 3:15-17 The Testimony of John the Baptist 3:18-20 John the Baptist Imprisoned 3:21-22 The Baptism of Jesus 3:23-38 The Genealogy of Jesus 4:1-13 The Temptation of Jesus 4:14-30 Jesus Rejected at Nazareth 4:31-37 Jesus Drives Out an Unclean Spirit 4:38-39 Jesus Heals Peter's Mother-in-Law 4:40-44 Jesus Heals Many and Withdraws to Pray 5:1-11 The Miraculous Catch of Fish 5:12-16 Jesus Cleanses a Leper 5:17-26 Jesus Heals a Paralytic 5:27-32 Jesus Calls Levi the Tax Collector 5:33-39 The Question About Fasting and New Wine 6:1-5 Jesus Is Lord of the Sabbath 6:6-11 Jesus Heals a Man with a Withered Hand on the Sabbath 6:12-16 Jesus Chooses the Twelve Apostles 6:17-26 Blessings and Woes on the Plain 6:27-36 Love Your Enemies 6:37-42 Do Not Judge 6:43-45 A Tree Is Known by Its Fruit 6:46-49 The House Built on the Rock 7:1-10 The Faith of the Centurion 7:11-17 Jesus Raises the Widow's Son at Nain 7:18-35 The Question of John the Baptist 7:36-50 A Sinful Woman's Love and Forgiveness 8:1-3 The Women Who Served Jesus 8:4-8 The Parable of the Sower 8:9-15 The Parable of the Sower Explained 8:16-18 A Lamp on a Stand 8:19-21 Jesus' True Family 8:22-25 Jesus Calms the Storm 8:26-39 Jesus Heals a Demon-Possessed Man at Gerasa 8:40-56 Jairus's Daughter and the Woman with the Issue of Blood 9:1-6 Jesus Sends Out the Twelve 9:7-9 Herod Hears About Jesus 9:10-17 Jesus Feeds the Five Thousand 9:18-21 Peter's Confession of Faith 9:22-27 Jesus Foretells His Suffering 9:28-36 The Transfiguration 9:37-43 Jesus Heals a Boy with an Unclean Spirit 9:44-45 Jesus Again Foretells His Death 9:46-50 Who Is the Greatest 9:51-56 A Samaritan Village Rejects Jesus 9:57-62 The Cost of Following Jesus 10:1-12 Jesus Sends Out the Seventy-Two 10:13-16 Woes on Unrepentant Towns 10:17-20 The Return of the Seventy-Two 10:21-24 Jesus Rejoices and Gives Thanks 10:25-37 The Parable of the Good Samaritan 10:38-42 Martha and Mary 11:1-13 Jesus Teaches on Prayer 11:14-23 Jesus and Beelzebul 11:24-28 The Generation That Seeks a Sign 11:29-32 The Sign of Jonah 11:33-36 The Lamp of the Body Is the Eye 11:37-54 Woes to the Pharisees and Lawyers 12:1-12 Beware of the Leaven of the Pharisees 12:13-21 The Parable of the Rich Fool 12:22-34 Do Not Be Anxious About Your Life 12:35-48 Watchful Servants 12:49-53 Jesus Came to Bring Division 12:54-59 Interpreting the Present Time 13:1-5 Repent or Perish 13:6-9 The Parable of the Barren Fig Tree 13:10-17 Jesus Heals a Crippled Woman on the Sabbath 13:18-19 The Parable of the Mustard Seed 13:20-21 The Parable of the Leaven 13:22-30 The Narrow Door 13:31-35 Lament Over Jerusalem 14:1-6 Jesus Heals a Man with Dropsy on the Sabbath 14:7-14 The Lesson of the Lowest Place 14:15-24 The Parable of the Great Banquet 14:25-35 The Cost of Discipleship 15:1-7 The Parable of the Lost Sheep 15:8-10 The Parable of the Lost Coin 15:11-32 The Parable of the Lost Son 16:1-13 The Parable of the Dishonest Manager 16:14-18 The Law and the Kingdom of God 16:19-31 The Rich Man and Lazarus 17:1-4 On Temptations to Sin and Forgiveness 17:5-10 Faith Like a Mustard Seed and the Servant's Duty 17:11-19 Jesus Cleanses Ten Lepers 17:20-37 The Coming of the Kingdom of God 18:1-8 The Parable of the Persistent Widow and the Unjust Judge 18:9-14 The Pharisee and the Tax Collector 18:15-17 Jesus Blesses the Little Children 18:18-30 The Rich Ruler 18:31-34 Jesus Foretells His Death a Third Time 18:35-43 Jesus Heals a Blind Beggar at Jericho 19:1-10 Jesus Calls Zacchaeus the Tax Collector 19:11-27 The Parable of the Ten Minas 19:28-40 The Triumphal Entry into Jerusalem 19:41-44 Jesus Weeps Over Jerusalem 19:45-48 Jesus Cleanses the Temple 20:1-8 The Authority of Jesus Questioned 20:9-19 The Parable of the Tenants 20:20-26 Paying Taxes to Caesar 20:27-40 The Question About the Resurrection 20:41-44 Whose Son Is the Christ 20:45-47 Beware of the Scribes 21:1-4 The Widow's Two Coins 21:5-36 The Olivet Discourse: Signs of the End 22:1-6 Judas Plots to Betray Jesus 22:7-13 Preparation of the Passover 22:14-20 The Institution of the Lord's Supper 22:21-23 Jesus Foretells His Betrayal 22:24-30 The Dispute About Who Is the Greatest 22:31-34 Jesus Foretells Peter's Denial 22:35-38 Purse, Bag, and Sword 22:39-46 Jesus Prays on the Mount of Olives 22:47-53 The Betrayal and Arrest of Jesus 22:54-62 Peter Denies Jesus 22:63-71 Jesus Before the Council 23:1-25 Jesus Before Pilate 23:26-43 The Crucifixion 23:44-49 The Death of Jesus 23:50-56 The Burial of Jesus 24:1-12 The Resurrection 24:13-35 On the Road to Emmaus 24:36-49 Jesus Appears to His Disciples 24:50-53 The Ascension
10:1
대기

Bayan haka, Ubangiji ya naɗa waɗansu mutum saba’in da biyu, ya aike su biyu-biyu, su riga shi yin gaba zuwa kowane gari da kowane wuri da zai shiga.

10:2
대기

Ya ce musu, “Girbi na da yawa, amma ma’aikata kaɗan ne. Saboda haka, ku roƙi Ubangijin girbi ya aikar da ma’aikata zuwa gonarsa.

10:3
대기

Ku tafi! Ina aikan ku kamar tumaki cikin kyarketai.

10:4
대기

Kada ku ɗauki jakar kuɗi, ko jaka, ko takalma. Kada ma ku gai da kowa a kan hanya.

10:5
대기

“Sa’ad da kuka shiga wani gida, ku fara da cewa, ‘Salama a gare ku mutanen gida.’

10:6
대기

In akwai mutum mai salama a gidan, salamarku za tă kasance tare da shi, in kuwa babu, salamarku za tă koma muku.

10:7
대기

Ku zauna a wannan gidan, kuna ci kuna shan duk abin da suka ba ku, gama ma’aikaci ya cancanci albashinsa. Kada ku yi yawan sāke masauƙi, daga gida zuwa gida.

10:8
대기

“Sa’ad da kuka shiga garin, kuma aka karɓe ku, ku ci ko mene ne da aka ajiye a gabanku.

10:9
대기

Ku warkar da marasa lafiya da suke wurin. Ku kuma faɗa musu cewa, ‘Mulkin Allah yana kusa da ku.’

10:10
대기

Amma sa’ad da kuka shiga garin, kuma ba a karɓe ku ba, ku bi titi-titi ku ce,

10:11
대기

‘Ko ƙurar garinku da kuke manne a ƙafafunmu, mun karkaɗe muku. Duk da haka, ku tabbatar da wannan, “Mulkin Allah yana kusa.” ’

10:12
대기

Ina dai faɗa muku, a ranan nan, za a fi jin tausayin Sodom fiye da wannan garin.

10:13
대기

“ ‘Kaitonki, Korazin! Kaitonki, Betsaida!’ Ai, da a ce a Taya da Sidon ne aka yi ayyukan banmamaki da aka yi a cikinku, da tuni sun tuba, suna zama cikin rigar makoki da toka.

10:14
대기

A ranar shari’a, za a fi jin tausayin Taya da Sidon fiye da ku.

10:15
대기

Ke kuma Kafarnahum, kina tsammani za ki sami ɗaukaka ne? A’a, za a hallaka ki.

10:16
대기

“Wanda ya saurare ku, ni yake saurara. Wanda ya ƙi ku, ni yake ƙi. Amma wanda ya ƙi ni kuwa, ya ƙi wanda ya aiko ni ne.”

10:17
대기

Mutum saba’in da biyun nan suka dawo da murna, suka ce, “Ubangiji, har mun sha ƙarfin aljanu ma a cikin sunanka.”

10:18
대기

Sai ya amsa ya ce, “Na ga Shaiɗan ya fāɗi daga sama kamar walƙiya.

10:19
대기

Na ba ku iko da za ku tattaka macizai, da kunamai, ku kuma shawo kan dukan ikon abokin gāba, kuma ba wani lahani da zai same ku.

10:20
대기

Duk da haka, kada ku yi farin ciki da cewa, kun sha ƙarfin ruhohi, amma ku yi farin ciki, domin an rubuta sunayenku a sama.”

10:21
대기

A wannan lokaci, Yesu, cike da murna ta wurin Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Na yabe ka, ya Uba, Ubangijin sama da ƙasa, domin ka ɓoye waɗannan abubuwa ga masu hikima, da masu ilimi, ka kuma bayyana su ga ƙananan yara. I, ya Uba, gama wannan shi ne nufinka mai kyau.

10:22
대기

“Ubana ya danƙa mini dukan kome. Ba wanda ya san Ɗan sai Uban, kuma ba wanda ya san Uban, sai Ɗan, da kuma waɗanda Ɗan ya zaɓa ya bayyana musu shi.”

10:23
대기

Sai ya juya wajen almajiransa, ya ce musu a ɓoye, “Albarka ga idanun da suka ga abin da kuke gani.

10:24
대기

Ina faɗa muku, annabawa da sarakuna da yawa sun so su ga abin nan da kuke gani, amma ba su gani ba. Sun so su ji abin da kuke ji, amma ba su ji ba.”

10:25
대기

Wata rana, sai wani masanin dokoki ya miƙe tsaye don yă gwada Yesu. Ya tambaya ya ce, “Malam, me zan yi don in gāji rai madawwami?”

10:26
대기

Yesu ya amsa ya ce, “Me aka rubuta a cikin Doka? Yaya kake karanta ta?”

10:27
대기

Sai ya amsa ya ce, “ ‘Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukan zuciyarka, da dukan ranka, da dukan ƙarfinka, da kuma dukan hankalinka’; kuma, ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’ ”

10:28
대기

Yesu ya ce, “Ka amsa daidai. Ka yi haka, kuma za ka rayu.”

10:29
대기

Amma domin ya kāre kansa, sai ya tambayi Yesu ya ce, “Shin, wane ne maƙwabcina?”

10:30
대기

Yesu ya amsa ya ce, “Wani mutum ya tashi daga Urushalima za shi Yeriko, sai ya fāɗi a hannun mafasa, wato, ’yan fashi. Suka ƙwace tufafinsa, suka yi masa dūka, suka bar shi nan bakin rai da mutuwa.

10:31
대기

Ya zamana wani firist ya bi kan wannan hanya. Da ya ga mutumin, sai ya bi gefe ya wuce abinsa.

10:32
대기

Haka ma wani daga kabilar Lawi, mai hidima cikin haikali, da ya zo wurin, ya gan shi, sai shi ma ya bi gefe ɗaya, ya wuce abinsa.

10:33
대기

Amma wani mutumin Samariya da yake kan tafiya, da ya kai inda mutumin yake, ya gan shi, sai ya ji tausayinsa.

10:34
대기

Ya je wurinsa, ya daddaure masa raunukansa, sa’an nan ya zuba mai, da ruwan inabi. Ya ɗauki mutumin ya sa a kan jakinsa, ya kai shi wani masauƙi, ya yi jinyarsa.

10:35
대기

Kashegari, sai ya ɗauki dinari biyu, ya ba wa mai masauƙin ya ce, ‘Ka lura da shi, bayan na dawo, zan biya ka duk abin da ka ƙara kashewa a kansa.’

10:36
대기

“A ganinka, a cikin waɗannan mutane uku, wane ne maƙwabcin mutumin da ya fāɗi a hannun mafasa?”

10:37
대기

Masanin dokoki ya amsa ya ce, “Wanda ya nuna masa jinƙai.”

10:38
대기

Yayinda Yesu da almajiransa suna cikin tafiya, sai ya kai wani ƙauye inda wata mace mai suna Marta ta marabce shi a gidanta.

10:39
대기

Tana da ’yar’uwa mai suna Maryamu, wadda ta zauna a gaban Ubangiji tana jin maganarsa.

10:40
대기

Marta kuwa, aikin hidima da ya kamata a yi, ya ɗauke mata hankali, sai ta zo wurin Yesu, ta ce, “Ubangiji, ba ka damu da yadda ’yar’uwata ta bar mini aiki ni kaɗai ba? Gaya mata ta taimake ni!”

10:41
대기

Amma Ubangiji ya amsa ya ce, “Marta, Marta, hankalinki ya tashi, kuma kina damuwa a kan abubuwa da yawa.

10:42
대기

Amma abu ɗaya tak ake bukata, Maryamu ta zaɓi abin da ya fi kyau, kuma ba za a raba ta da shi ba.”