scripture.how 성경필사
KO

Copywork

Hausa BSRK 누가복음 22장

성경필사는 빠르게 끝내는 입력 훈련이 아니라, 한 절씩 말씀의 문장과 흐름을 다시 붙드는 시간입니다. 입력 내용은 이 브라우저에 임시 저장되며, 로그인하면 계정에도 저장됩니다.

KO 한국어
ZH 중국어
JA 일본어
HI 힌디어
BN 벵골어
TA 타밀어
TE 텔루구어
ML 말라얄람어
FA 페르시아어
MY 버마어
NE 네팔어
MR 마라티어
KN 칸나다어
HA 하우사어
YO 요루바어
SW 스와힐리어
IG 이그보어
ID 인도네시아어
TSI
PT 포르투갈어
VI 베트남어
AR 아랍어
AVD
RU 러시아어
UK 우크라이나어
RO 루마니아어
BTF
IT 이탈리아어
FI 핀란드어
TO 통가어
HR 크로아티아어
SR 세르비아어
TR 튀르키예어
HU 헝가리어
PL 폴란드어
SK 슬로바키아어
LA 라틴어
NL 네덜란드어
CS 체코어
FR 프랑스어
ES 스페인어
DE 독일어
ETC 기타 언어

소제목 단위로 진행 · 누가복음

1:1-4 Dedication to Theophilus 1:5-25 The Birth of John the Baptist Foretold 1:26-38 The Birth of Jesus Foretold 1:39-45 Mary Visits Elizabeth 1:46-56 Mary's Song of Praise: The Magnificat 1:57-66 The Birth of John the Baptist 1:67-80 Zechariah's Prophecy 2:1-7 The Birth of Jesus in Bethlehem 2:8-20 The Shepherds and the Angels 2:21-24 Jesus Presented in the Temple 2:25-35 Simeon Holds the Child 2:36-40 The Testimony of the Prophetess Anna 2:41-52 The Boy Jesus in the Temple 3:1-14 John the Baptist Prepares the Way 3:15-17 The Testimony of John the Baptist 3:18-20 John the Baptist Imprisoned 3:21-22 The Baptism of Jesus 3:23-38 The Genealogy of Jesus 4:1-13 The Temptation of Jesus 4:14-30 Jesus Rejected at Nazareth 4:31-37 Jesus Drives Out an Unclean Spirit 4:38-39 Jesus Heals Peter's Mother-in-Law 4:40-44 Jesus Heals Many and Withdraws to Pray 5:1-11 The Miraculous Catch of Fish 5:12-16 Jesus Cleanses a Leper 5:17-26 Jesus Heals a Paralytic 5:27-32 Jesus Calls Levi the Tax Collector 5:33-39 The Question About Fasting and New Wine 6:1-5 Jesus Is Lord of the Sabbath 6:6-11 Jesus Heals a Man with a Withered Hand on the Sabbath 6:12-16 Jesus Chooses the Twelve Apostles 6:17-26 Blessings and Woes on the Plain 6:27-36 Love Your Enemies 6:37-42 Do Not Judge 6:43-45 A Tree Is Known by Its Fruit 6:46-49 The House Built on the Rock 7:1-10 The Faith of the Centurion 7:11-17 Jesus Raises the Widow's Son at Nain 7:18-35 The Question of John the Baptist 7:36-50 A Sinful Woman's Love and Forgiveness 8:1-3 The Women Who Served Jesus 8:4-8 The Parable of the Sower 8:9-15 The Parable of the Sower Explained 8:16-18 A Lamp on a Stand 8:19-21 Jesus' True Family 8:22-25 Jesus Calms the Storm 8:26-39 Jesus Heals a Demon-Possessed Man at Gerasa 8:40-56 Jairus's Daughter and the Woman with the Issue of Blood 9:1-6 Jesus Sends Out the Twelve 9:7-9 Herod Hears About Jesus 9:10-17 Jesus Feeds the Five Thousand 9:18-21 Peter's Confession of Faith 9:22-27 Jesus Foretells His Suffering 9:28-36 The Transfiguration 9:37-43 Jesus Heals a Boy with an Unclean Spirit 9:44-45 Jesus Again Foretells His Death 9:46-50 Who Is the Greatest 9:51-56 A Samaritan Village Rejects Jesus 9:57-62 The Cost of Following Jesus 10:1-12 Jesus Sends Out the Seventy-Two 10:13-16 Woes on Unrepentant Towns 10:17-20 The Return of the Seventy-Two 10:21-24 Jesus Rejoices and Gives Thanks 10:25-37 The Parable of the Good Samaritan 10:38-42 Martha and Mary 11:1-13 Jesus Teaches on Prayer 11:14-23 Jesus and Beelzebul 11:24-28 The Generation That Seeks a Sign 11:29-32 The Sign of Jonah 11:33-36 The Lamp of the Body Is the Eye 11:37-54 Woes to the Pharisees and Lawyers 12:1-12 Beware of the Leaven of the Pharisees 12:13-21 The Parable of the Rich Fool 12:22-34 Do Not Be Anxious About Your Life 12:35-48 Watchful Servants 12:49-53 Jesus Came to Bring Division 12:54-59 Interpreting the Present Time 13:1-5 Repent or Perish 13:6-9 The Parable of the Barren Fig Tree 13:10-17 Jesus Heals a Crippled Woman on the Sabbath 13:18-19 The Parable of the Mustard Seed 13:20-21 The Parable of the Leaven 13:22-30 The Narrow Door 13:31-35 Lament Over Jerusalem 14:1-6 Jesus Heals a Man with Dropsy on the Sabbath 14:7-14 The Lesson of the Lowest Place 14:15-24 The Parable of the Great Banquet 14:25-35 The Cost of Discipleship 15:1-7 The Parable of the Lost Sheep 15:8-10 The Parable of the Lost Coin 15:11-32 The Parable of the Lost Son 16:1-13 The Parable of the Dishonest Manager 16:14-18 The Law and the Kingdom of God 16:19-31 The Rich Man and Lazarus 17:1-4 On Temptations to Sin and Forgiveness 17:5-10 Faith Like a Mustard Seed and the Servant's Duty 17:11-19 Jesus Cleanses Ten Lepers 17:20-37 The Coming of the Kingdom of God 18:1-8 The Parable of the Persistent Widow and the Unjust Judge 18:9-14 The Pharisee and the Tax Collector 18:15-17 Jesus Blesses the Little Children 18:18-30 The Rich Ruler 18:31-34 Jesus Foretells His Death a Third Time 18:35-43 Jesus Heals a Blind Beggar at Jericho 19:1-10 Jesus Calls Zacchaeus the Tax Collector 19:11-27 The Parable of the Ten Minas 19:28-40 The Triumphal Entry into Jerusalem 19:41-44 Jesus Weeps Over Jerusalem 19:45-48 Jesus Cleanses the Temple 20:1-8 The Authority of Jesus Questioned 20:9-19 The Parable of the Tenants 20:20-26 Paying Taxes to Caesar 20:27-40 The Question About the Resurrection 20:41-44 Whose Son Is the Christ 20:45-47 Beware of the Scribes 21:1-4 The Widow's Two Coins 21:5-36 The Olivet Discourse: Signs of the End 22:1-6 Judas Plots to Betray Jesus 22:7-13 Preparation of the Passover 22:14-20 The Institution of the Lord's Supper 22:21-23 Jesus Foretells His Betrayal 22:24-30 The Dispute About Who Is the Greatest 22:31-34 Jesus Foretells Peter's Denial 22:35-38 Purse, Bag, and Sword 22:39-46 Jesus Prays on the Mount of Olives 22:47-53 The Betrayal and Arrest of Jesus 22:54-62 Peter Denies Jesus 22:63-71 Jesus Before the Council 23:1-25 Jesus Before Pilate 23:26-43 The Crucifixion 23:44-49 The Death of Jesus 23:50-56 The Burial of Jesus 24:1-12 The Resurrection 24:13-35 On the Road to Emmaus 24:36-49 Jesus Appears to His Disciples 24:50-53 The Ascension
22:1
대기

Yanzu fa, Bikin Burodi Marar Yistin da ake kira Bikin Ƙetarewa ya yi kusa,

22:2
대기

manyan firistoci da malaman dokoki kuma suna neman yadda za su kashe Yesu a ɓoye, don suna tsoron mutane.

22:3
대기

Shaiɗan kuwa ya shiga Yahuda, wanda ake kira Iskariyot, ɗaya daga cikin Sha Biyun.

22:4
대기

Sai Yahuda ya je ya tattauna da manyan firistoci, da ma’aikatan ’yan gadin haikali, a kan yadda zai ba da Yesu a gare su.

22:5
대기

Suka kuwa yi murna, suka yarda su ba shi kuɗi.

22:6
대기

Ya ko yarda, ya fara neman zarafin da zai ba da Yesu a gare su, sa’ad da taro ba sa nan tare da shi.

22:7
대기

Sai ranar Bikin Burodi Marar Yisti ta kewayo, wato, ranar hadayar ɗan ragon kafara na Bikin Ƙetarewa.

22:8
대기

Sai Yesu ya aiki Bitrus da Yohanna, ya ce musu, “Ku je ku yi shirye-shiryen Bikin Ƙetarewar da za mu ci.”

22:9
대기

Suka tambaye shi suka ce, “Ina kake so mu je mu yi shirin?”

22:10
대기

Ya amsa ya ce, “Sa’ad da kuka shiga cikin gari, za ku sadu da wani mutum yana ɗauke da tulun ruwa. Ku bi shi zuwa gidan da zai shiga.

22:11
대기

Ku ce wa maigidan, Malam ya aike mu mu ce maka, ‘Ina ɗakin baƙi, inda ni da almajiraina za mu ci abincin Bikin Ƙetarewa?’

22:12
대기

Zai nuna muku wani babban ɗakin sama a shirye. Nan za ku yi shirin.”

22:13
대기

Sai suka tafi, suka kuma iske kome kamar yadda Yesu ya faɗa musu. Sai suka shirya Bikin Ƙetarewa.

22:14
대기

Da lokaci ya yi, sai Yesu ya zauna tare da manzanninsa don cin abinci.

22:15
대기

Sai ya ce musu, “Na yi marmari ƙwarai don in ci wannan Bikin Ƙetarewa tare da ku, kafin in sha wahala.

22:16
대기

Ina dai gaya muku, ba zan ƙara cinsa ba, sai ya sami cika a mulkin Allah.”

22:17
대기

Bayan ya ɗauki kwaf ruwan inabi, ya yi godiya, sai ya ce, “Ku karɓa, ku rarraba wa junanku.

22:18
대기

Ina dai gaya muku, ba zan ƙara sha daga ’ya’yan inabi ba, sai mulkin Allah ya zo.”

22:19
대기

Sai ya ɗauki burodi ya yi godiya, ya kakkarya ya ba su, da cewa, “Wannan jikina ne, da aka bayar dominku. Ku riƙa yin haka don tunawa da ni.”

22:20
대기

Haka kuma, bayan abincin, ya ɗauki kwaf ruwan inabi ya ce, “Wannan kwaf ruwan inabi shi ne, na sabon alkawari cikin jinina, da aka zubar dominku.

22:21
대기

Amma hannun wanda zai ci amanata, yana cin abincin tare da ni.

22:22
대기

Ɗan Mutum zai mutu kamar yadda aka ƙaddara, amma kaiton mutumin da zai bashe shi.”

22:23
대기

Sai suka fara tambayar junansu, ko wane ne a cikinsu zai yi wannan.

22:24
대기

Gardama ta tashi a tsakaninsu, a kan ko wane ne a cikinsu ya fi girma.

22:25
대기

Yesu ya ce musu, “Sarakunan Al’ummai suna nuna iko a kan mutanensu, kuma waɗanda suke nuna iko a kansu, suna kiran kansu Masu Taimakon mutane.

22:26
대기

Amma ku, kada ku zama haka. A maimakon haka, sai dai wanda ya fi girma a cikinku, ya zama kamar wanda ya fi ƙanƙanta, wanda kuma ke mulki, ya zama kamar mai hidima.

22:27
대기

Wane ne ya fi girma? Wanda yake zaune a tebur ne, ko kuma shi da yake yin hidima? Ashe, ba wanda yake zaune a tebur ba ne? Amma ga ni, ni mai yin hidima ne a cikinku.

22:28
대기

Ku ne kuka tsaya tare da ni a gwaje-gwajen da na sha.

22:29
대기

Daidai kamar yadda Ubana ya ba ni mulki, haka ni ma nake ba ku.

22:30
대기

Saboda ku ci, ku sha a teburina a cikin mulkina. Kuma ku zauna a kan gadon sarauta, ku yi wa kabilu goma sha biyu na Isra’ila shari’a.

22:31
대기

“Siman, Siman, Shaiɗan ya nemi izini ya sheƙe ka kamar alkama.

22:32
대기

Amma na yi maka addu’a, Siman, domin kada bangaskiyarka ta kāsa. Bayan ka juyo, ka ƙarfafa ’yan’uwanka.”

22:33
대기

Amma ya amsa ya ce, “Ubangiji, ina a shirye in tafi tare da kai har kurkuku, ko mutuwa ma.”

22:34
대기

Yesu ya ce, “Ina gaya maka Bitrus, kafin zakara ya yi cara yau, za ka yi mūsun sanina sau uku.”

22:35
대기

Sai Yesu ya tambaye, su ya ce, “Lokacin da na aike ku ba tare da jakar kuɗi, ko jaka, ko takalma ba, kun rasa wani abu?”

22:36
대기

Ya ce musu, “Amma yanzu, in kuna da jakar kuɗi, ko jaka, ku ɗauka. In kuma ba ku da takobi, ku sayar da rigarku, ku saya.

22:37
대기

A rubuce yake cewa, ‘An lissafta shi tare da masu zunubi.’ Ina kuwa gaya muku, dole wannan ya cika a kaina. I, abin da aka rubuta a kaina yana kusan cikawa.”

22:38
대기

Almajiran suka ce, “Duba Ubangiji, ga takuba biyu.”

22:39
대기

Yesu ya fita zuwa Dutsen Zaitun kamar yadda ya saba, almajiransa kuma suka bi shi.

22:40
대기

Da ya kai wurin, sai ya ce musu, “Ku yi addu’a don kada ku fāɗi cikin jarraba.”

22:41
대기

Sai ya janye daga wurinsu, misalin nisan jifa, ya durƙusa a ƙasa ya yi addu’a,

22:42
대기

“Uba, in ka yarda, ka ɗauke mini wannan kwaf, amma ba nufina ba, sai dai naka.”

22:43
대기

Wani mala’ika daga sama ya bayyana gare shi, ya ƙarfafa shi.

22:44
대기

Domin tsananin azaba, sai ya ƙara himma cikin addu’a, zuffansa kuma na ɗigowa ƙasa kamar jini.

22:45
대기

Da ya tashi daga addu’a, ya koma inda almajiransa suke, sai ya iske su suna barci, daga gajiyar baƙin ciki.

22:46
대기

Ya tambaye su, “Don me kuke barci? Ku tashi ku yi addu’a, don kada ku fāɗi cikin jarraba.”

22:47
대기

Yana cikin magana sai ga taro sun zo. Mutumin nan da ake kira Yahuda, ɗaya daga cikin Sha Biyun, shi ya bi da su. Sai ya matso kusa da Yesu don yă yi masa sumba.

22:48
대기

Amma Yesu ya tambaye shi ya ce, “Yahuda, ashe, da sumba za ka bashe Ɗan Mutum?”

22:49
대기

Da masu bin Yesu suka ga abin da zai faru, sai suka ce, “Ubangiji, mu yi sara da takubanmu ne?”

22:50
대기

Sai ɗayansu ya kai sara ga bawan babban firist, ya sare kunnen damansa.

22:51
대기

Amma Yesu ya amsa ya ce, “Kada a ƙara yin wannan!” Sai ya taɓa kunnen mutumin da aka sara, ya warkar da shi.

22:52
대기

Sai Yesu ya ce wa manyan firistoci, da ma’aikatan ’yan gadin haikali, da dattawa, waɗanda suka zo don su kama shi, “Ina jagoran wani tawaye ne, da za ku zo da takuba da sanduna?

22:53
대기

Kullum ina tare da ku a filin haikali, amma ba ku kama ni ba. Amma wannan ne sa’a naku, lokacin da duhu yake mulki.”

22:54
대기

Sai suka kama shi suka kai shi gidan babban firist. Bitrus ya bi su daga nesa.

22:55
대기

Amma da suka hura wuta a tsakiyar harabar gidan, kowa ya zauna, sai Bitrus ya zo ya zauna tare da su.

22:56
대기

Wata baiwa ta gan shi zaune kusa da wutar. Ta dube shi sosai sa’an nan, ta ce, “Ai, wannan mutum ma yana tare da shi.”

22:57
대기

Amma ya yi mūsu ya ce, “Mace, ban san shi ba!”

22:58
대기

Bayan ɗan lokaci kaɗan, wani dabam ya gan shi ya ce, “Kai ma ɗayansu ne.”

22:59
대기

Bayan kamar sa’a ɗaya, sai wani mutum ya ce, “Ba shakka, mutumin nan ma yana tare da shi, don shi mutumin Galili ne.”

22:60
대기

Bitrus ya amsa ya ce, “Kai, ban ma san abin da kake magana a kai ba!” Yana cikin magana, sai zakara ya yi cara.

22:61
대기

Ubangiji kuma ya juya ya kafa wa Bitrus ido. Sai Bitrus ya tuna da maganar da Ubangiji ya ce masa, “Kafin zakara ya yi cara yau, za ka yi mūsun sanina sau uku.”

22:62
대기

Sai ya fita waje, ya yi kuka mai zafi.

22:63
대기

Mutanen da suke gadin Yesu suka fara masa ba’a da dūka.

22:64
대기

Suka rufe masa idanu suna tambaya cewa, “Ka yi annabci! Wa ya mare ka?”

22:65
대기

Suka kuma yi masa waɗansu baƙaƙen maganganu masu yawa.

22:66
대기

Da gari ya waye, sai majalisar dattawa na mutane, da manyan firistoci, da malaman dokoki, suka taru wuri ɗaya. Sai aka kawo Yesu a gabansu.

22:67
대기

Suka ce, “Ka faɗa mana, ko kai ne Kiristi?”

22:68
대기

in kuma na yi muku tambaya ba za ku iya ba ni amsa ba.

22:69
대기

Amma daga yanzu, Ɗan Mutum zai zauna a hannun dama na Allah Mai Iko.”

22:70
대기

Sai dukansu suka yi tambaya suka ce, “Wato, kai Ɗan Allah ke nan?”

22:71
대기

Sai suka ce, “Wace shaida kuma muke nema? Ai, mun ji abin da ya ce da bakinsa.”