scripture.how 성경필사
KO

Copywork

Hausa BSRK 마가복음 5장

성경필사는 빠르게 끝내는 입력 훈련이 아니라, 한 절씩 말씀의 문장과 흐름을 다시 붙드는 시간입니다. 입력 내용은 이 브라우저에 임시 저장되며, 로그인하면 계정에도 저장됩니다.

KO 한국어
ZH 중국어
JA 일본어
HI 힌디어
BN 벵골어
TA 타밀어
TE 텔루구어
ML 말라얄람어
FA 페르시아어
MY 버마어
NE 네팔어
MR 마라티어
KN 칸나다어
HA 하우사어
YO 요루바어
SW 스와힐리어
IG 이그보어
ID 인도네시아어
TSI
PT 포르투갈어
VI 베트남어
AR 아랍어
AVD
RU 러시아어
UK 우크라이나어
RO 루마니아어
BTF
IT 이탈리아어
FI 핀란드어
TO 통가어
HR 크로아티아어
SR 세르비아어
TR 튀르키예어
HU 헝가리어
PL 폴란드어
SK 슬로바키아어
LA 라틴어
NL 네덜란드어
CS 체코어
FR 프랑스어
ES 스페인어
DE 독일어
ETC 기타 언어

소제목 단위로 진행 · 마가복음

1:1-6 The Beginning of the Gospel and the Cry of John the Baptist 1:7-8 The Testimony of John the Baptist 1:9-11 The Baptism of Jesus 1:12-13 The Temptation in the Wilderness 1:14-15 Jesus Proclaims the Kingdom of God in Galilee 1:16-20 Jesus Calls Four Fishermen as Disciples 1:21-28 Jesus Drives Out an Unclean Spirit in the Synagogue 1:29-31 Jesus Heals Peter's Mother-in-Law 1:32-34 Jesus Heals Many at Evening 1:35-39 Prayer in a Solitary Place and a Preaching Tour 1:40-45 Jesus Cleanses a Leper 2:1-12 Jesus Heals a Paralytic 2:13-17 The Calling of Matthew the Tax Collector 2:18-22 A Question About Fasting and the Parable of New Wine 2:23-28 Jesus Passes Through the Grainfields on the Sabbath 3:1-6 Jesus Heals a Man with a Withered Hand on the Sabbath 3:7-12 Great Crowds Gather by the Sea 3:13-19 Jesus Appoints the Twelve Disciples 3:20-21 The Family Who Tried to Seize Jesus 3:22-30 The Beelzebul Controversy 3:31-35 Who Are Jesus' True Family 4:1-9 The Parable of the Sower 4:10-12 The Reason for Speaking in Parables 4:13-20 Jesus Explains the Parable of the Sower 4:21-25 Lessons of the Lamp and the Measure 4:26-29 The Parable of the Growing Seed 4:30-32 The Parable of the Mustard Seed 4:33-34 The Conclusion on Teaching in Parables 4:35-41 Jesus Calms the Storm 5:1-20 The Gerasene Demoniac 5:21-43 Jairus' Daughter and the Woman with a Hemorrhage 6:1-6 Jesus Rejected at Nazareth 6:7-13 Jesus Sends Out the Twelve 6:14-29 Herod's News and the Death of John the Baptist 6:30-44 Jesus Feeds the Five Thousand 6:45-52 Jesus Walks on the Water 6:53-56 Jesus Heals the Sick at Gennesaret 7:1-13 Jesus Rebukes the Tradition of the Elders 7:14-23 What Truly Defiles a Person 7:24-30 The Faith of the Syrophoenician Woman 7:31-37 Jesus Heals a Deaf and Mute Man 8:1-10 Jesus Feeds the Four Thousand 8:11-13 The Pharisees Demand a Sign 8:14-21 Beware the Leaven of the Pharisees and Herod 8:22-26 Jesus Heals a Blind Man at Bethsaida 8:27-30 Peter's Confession of Faith 8:31-33 Jesus Foretells His Suffering and Death for the First Time 8:34-38 Deny Yourself and Take Up Your Cross 9:1 The Kingdom of God Coming in Power 9:2-10 The Transfiguration 9:11-13 The Question About Elijah Coming First 9:14-29 Jesus Heals a Boy with an Unclean Spirit 9:30-32 Jesus Foretells His Death and Resurrection a Second Time 9:33-37 Who Is the Greatest 9:38-41 Whoever Is Not Against Us Is for Us 9:42-50 A Warning Against Causing Others to Stumble 10:1-12 Teaching on Divorce 10:13-16 Jesus Blesses the Little Children 10:17-31 The Rich Young Man 10:32-34 Jesus Foretells His Suffering a Third Time 10:35-45 The Request of James and John and the Way of Service 10:46-52 Jesus Heals Blind Bartimaeus at Jericho 11:1-11 The Triumphal Entry into Jerusalem 11:12-14 Jesus Curses the Fig Tree 11:15-19 Jesus Cleanses the Temple 11:20-26 The Withered Fig Tree and the Prayer of Faith 11:27-33 By What Authority Are You Doing These Things 12:1-12 The Parable of the Tenants 12:13-17 Paying Taxes to Caesar 12:18-27 The Sadducees Dispute About the Resurrection 12:28-34 The Greatest Commandment 12:35-37 Is the Christ the Son of David 12:38-40 A Warning Against the Scribes 12:41-44 The Widow's Two Coins 13:1-37 The Olivet Discourse (Signs of the End) 14:1-2 The Plot to Kill Jesus 14:3-9 Mary Anoints Jesus with Perfume 14:10-11 Judas Agrees to Betray Jesus 14:12-16 Preparing the Passover Meal 14:17-21 Jesus Foretells His Betrayal 14:22-26 The Institution of the Lord's Supper 14:27-31 Jesus Foretells Peter's Denial 14:32-42 Jesus Prays in Gethsemane 14:43-52 The Arrest of Jesus 14:53-65 Jesus Before the Sanhedrin 14:66-72 Peter Denies Jesus 15:1-15 Jesus Before Pilate 15:16-20 The Soldiers Mock Jesus 15:21-32 The Crucifixion 15:33-41 The Death of Jesus 15:42-47 The Burial of Jesus 16:1-8 The Resurrection 16:9-11 Jesus Appears to Mary Magdalene 16:12-13 Jesus Appears to Two Disciples 16:14-18 Jesus Appears to the Eleven and Commissions the Gospel 16:19-20 Jesus Is Taken Up to Heaven and the Disciples Preach
5:1
대기

Suka ƙetare tafkin suka je yankin Gerasenawa.

5:2
대기

Da Yesu ya sauka daga jirgin ruwa, sai wani mutum mai mugun ruhu ya fito daga kaburbura, ya tarye shi.

5:3
대기

Wannan mutumin ya mai da kaburbura gidansa. Kuma ba wanda ya iya daure shi, ko da sarƙa ma.

5:4
대기

Gama an sha daure shi hannu da ƙafa da sarƙa, amma yakan tsintsinke sarƙar, yă kuma karye ƙarafan da suke ƙafafunsa. Ba wanda yake da ƙarfin da zai iya yă riƙe shi.

5:5
대기

Dare da rana, sai yă dinga kuka yana ƙuƙƙuje jikinsa da duwatsu a cikin kaburbura da kan tuddai.

5:6
대기

Da ya hangi Yesu daga nesa, sai ya ruga da gudu, ya zo ya durƙusa a gabansa.

5:7
대기

Ya yi ihu da babbar murya ya ce, “Ina ruwanka da ni Yesu, Ɗan Allah Mafi Ɗaukaka? Ka rantse da Allah cewa ba za ka ba ni azaba ba!”

5:8
대기

Gama Yesu ya riga ya ce masa, “Ka fita daga jikin mutumin nan, kai mugun ruhu!”

5:9
대기

Sai Yesu ya tambaye shi ya ce, “Mene ne sunanka?”

5:10
대기

Sai ya yi ta roƙon Yesu, kada yă kore su daga wurin.

5:11
대기

A kan tudun da yake nan kusa kuwa, akwai wani babban garken aladu, suna kiwo.

5:12
대기

Sai aljanun suka roƙi Yesu, suka ce, “Tura mu cikin aladun nan, ka bari mu shiga cikinsu.”

5:13
대기

Ya kuwa yarda musu, sai mugayen ruhohin suka fita suka shiga cikin aladun. Garken kuwa, yana da kusan aladu dubu biyu, suka gangara daga kan tudun zuwa cikin tafkin, suka nutse.

5:14
대기

Masu kiwon aladun kuwa suka ruga da gudu zuwa cikin gari da ƙauyuka, suka ba da wannan labari. Sai mutanen suka fito, domin su ga abin da ya faru.

5:15
대기

Da suka kai wajen Yesu, sai suka ga mutumin da dā yake da tulin aljanun yana zaune a wurin, sanye da tufafi kuma cikin hankalinsa, sai suka ji tsoro.

5:16
대기

Waɗanda suka ga abin da ya faru, suka ba da labarin abin da ya faru da mai aljanun, da kuma aladun.

5:17
대기

Sai mutane suka fara roƙon Yesu yă bar yankinsu.

5:18
대기

Yesu yana kan shiga cikin jirgin ruwa ke nan, sai mutumin da dā yake da aljanun ya roƙa yă bi shi.

5:19
대기

Yesu bai yardar masa ba, amma ya ce, “Ka tafi gida wurin iyalinka, ka gaya musu babban alherin da Ubangiji ya yi maka, da yadda ya yi maka jinƙai.”

5:20
대기

Sai mutumin ya tafi, ya yi ta ba da labari a cikin Dekafolis a kan babban alherin da Yesu ya yi masa. Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.

5:21
대기

Da Yesu ya sāke ƙetarewa cikin jirgin ruwa zuwa ɗaya hayen tafkin, sai taro mai yawa ya taru kewaye da shi yayinda yake a bakin tafkin.

5:22
대기

Sai ɗaya a cikin masu mulkin majami’a, wanda ake kira Yayirus ya zo wurin. Da ganin Yesu, sai ya durƙusa a gabansa,

5:23
대기

ya roƙe shi da gaske ya ce, “Ƙaramar diyata tana bakin mutuwa. In ka yarda, ka zo ka ɗibiya hannunka a kanta, domin ta warke, ta kuma rayu.”

5:24
대기

Sai Yesu ya tafi tare da shi.

5:25
대기

A can kuwa akwai wata mace, wadda ta yi shekaru goma sha biyu tana zub da jini.

5:26
대기

Ta kuma sha wahala ƙwarai a hannun likitoci da yawa, har ta kashe duk abin da take da shi, amma maimakon samun sauƙi, sai ciwon ya ƙara muni.

5:27
대기

Da ta ji labarin Yesu, sai ta zo ta bayansa, a cikin taron, ta taɓa rigarsa,

5:28
대기

domin ta yi tunani cewa, “Ko da rigunarsa ma na taɓa, zan warke.”

5:29
대기

Nan da take, zub da jininta ya tsaya, sai ta ji a jikinta ta rabu da shan wahalarta.

5:30
대기

Nan da nan Yesu ya gane cewa, iko ya fita daga gare shi. Sai ya juya a cikin taron ya yi tambaya, “Wa ya taɓa rigata?”

5:31
대기

Sai almajiransa suka ce, “Kana ganin mutane suna matsinka, duk da haka kana tambaya, ‘Wa ya taɓa ni?’ ”

5:32
대기

Amma Yesu ya ci gaba da dubawa don yă ga wa ya taɓa shi.

5:33
대기

Matar, da yake ta san abin da ya faru da ita, sai ta zo ta durƙusa a gabansa, da tsoro da rawan jiki, ta kuma gaya masa dukan abin da ya faru.

5:34
대기

Sai ya ce mata, “Diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya, kin kuma rabu da dukan wahalarki.”

5:35
대기

Yayinda Yesu yana cikin magana, sai waɗansu mutane daga gidan Yayirus, mai mulkin majami’a, suka zo suka ce, “Diyarka ta rasu. Kada ma ka wahal da Malam.”

5:36
대기

Yesu bai kula da abin da suka faɗa ba, sai ya ce wa mai mulkin majami’ar, “Kada ka ji tsoro, ka gaskata kawai.”

5:37
대기

Bai bar kowa ya bi shi ba, sai Bitrus, Yaƙub da Yohanna ɗan’uwan Yaƙub.

5:38
대기

Da suka iso gidan mai mulkin majami’ar, sai Yesu ya ga ana hayaniya, mutane suna kuka da kururuwa.

5:39
대기

Sai ya shiga ciki, ya ce musu, “Mene ne dalilin wannan hayaniya da kuka? Yarinyar ba mutuwa ne ta yi ba, barci take yi.”

5:40
대기

Sai suka yi masa dariya.

5:41
대기

Sai ya kama hannunta ya ce mata, “Talita kum!” (Wato, “Ƙaramar yarinya, na ce miki, tashi!”).

5:42
대기

Nan da nan, sai yarinyar ta tashi ta yi tafiya (shekarunta goma sha biyu ne). Saboda wannan, suka yi mamaki ƙwarai.

5:43
대기

Sai ya ba da umarni mai tsanani, kada kowa yă san kome game da wannan. Sai ya ce musu, su ba ta wani abu tă ci.